rαѕhín hαlαrtα zαnα ízαr hαfѕαn ѕσjαn ѕαmα чα ѕα чαn nαjєríчα ѕunчíwα ѕhugαвαn kαѕαr chα

 

Yan Najeriya musamman a kafafen sada zamunta sun yi ca akan shugaban Najeriya Muhammadu Buhari da mataimakinsa Farfesa Yemi Osinbajo, saboda kin halartar jana’izar babban hafsan sojin kasar da wasu sojoji da suka mutu a hatsarin jirgin sama.



Laftanar Janar Attahiru ya rasu a ranar Juma’a 21 ga watan Mayu, tare da wasu sojoji 10 yayin da suke kan hanyarsu ta zuwa Kaduna daga Abuja.

Jirgin ya fadi ne a kusa da filin tashin jirage na kasa da kasa da ke Kaduna.

An yi jana’izarsu a ranar Asabar 22 ga watan Mayu, a makabartar dakarun kasar da ke Abuja, babban birnin Najeriya.

Sai dai rashin halartar shugabannin biyu, ya janyo ce-ce-ku-ce a tsakanin ‘yan Najeriya, inda jama’a da dama suka raja’a akan cewa kin halartar jana’izar bai dace ba.