Amnesty International : || Ta Tabbatar Wa Hukumomin Najeriya Basa Wani Motsi Wajen Kare Rayukan Yan Nigeria

 

                    ᗩᗰᑎᗴᔕ丅Ƴ Ꭵᑎ丅ᗴᖇᑎᗩ丅Ꭵᗝᑎᗩᒪ

https://www.facebook.com/zinariyadailytrust/




A wata sanarwa da ƙungiyar ta fitar albarkacin cikarta shekara 60 da fara aiki a Najeriya, ta kuma ce waɗannan abubuwa na nuna tsabar gazawar hukumomi wajen kare rayuka da dukiyar al'umma.

Ƙungiyar ta ce ta fara aiki ne ranar 1 ga watan Yunin 1967 da wani ƙoƙari lokacin yaƙin basasar Najeriya ta hanyar ayyana Wole Soyinka, mutumin da ya samu kyautar Nobel, a matsayin fursunan da aka ɗaure saboda aƙidarsa.

Amnesty ta ce tsakanin 1968 zuwa 1969 rahotonta na shekara-shekara ya bayyana damuwa kan yadda ake jingina haƙƙin ɗan adam a Najeriya da sunan yaƙin basasa.

Ta kuma ce babu wani ƙwaƙƙwaran sauyi ta fuskar kare haƙƙin ɗan adam da aka samu tun daga 1967.

"Kashe-kashe ba ji ba gani da gaza kawo ƙarshensu da hukunta mutanen da ake zargi da laifi na ci gaba da zama barazana ga ƴancin rayuwa a Najeriya," in ji sanarwar ta Ammnesty.

Daraktar Amnesty a Najeriya Osai Ojigho, ta ce daga mulkin kama karya na zamanin sojoji har zuwa mulkin farar hula a yau, ana keta haƙƙin ƴan adam da kuma tozarta ƴan ƙasa.